IQNA

An Karrama Wadanda Suka Gudanar Da Gasar Kur’ani A Saliyo

23:49 - May 29, 2018
Lambar Labari: 3482705
Bangaren kasa da kasa, an girmama wadanda suka gudana da gasar kur’ai mai tsarki ta kasar Saliyo.

 

Kamfanin dillancin labaran iqna ya habarta cewa, ya nakalto daga shafin sadarwa na yanar gizo na cibiyar yada al’adun musulunci cewa, a jiya an girmama wadanda suka gudana da gasar kur’ai mai tsarki ta kasar Saliyo  abirnin Freetown fadar mulkin kasar.

A yayin taron na jiya an bayar da kyautuka ga dukkanin wadada suka halarci wannan gasa, da kuma kyautuka na musamman ga wadanda suka nuna kwazo.

Ali Reza Faramarzi shugaban karamin ofishin jakadancin Iran shi ne ya bude taron da karatun surat qadr.

Kasar Iran ce dai ta dauki nauyin dukkanin abubuwan da aka kasashe a yayin gudanar da wannan gasar kur’ani ta kasar Saliyo.

Maisami Zadeh shugaban jami’ar almustafa a kasar ya bayyana cewa, wannan gasa tana da matukar muhimmanci.

Haka nan kuma an nuna karatun wasu daga cikin fitattun makaranta kur’ani Iraniyawa da suka hada da Jawad Forughi.

3718641

 

 

 

 

 

captcha