IQNA

Haramta Hizbullah Da Birtaniya Ya Sabawa Dokokin Kasar

22:31 - February 26, 2019
Lambar Labari: 3483404
Bangaren kasa da kasa, kungiyoyin kare hakkin bil adama a kasashen duniya suna ci gaba da mayarwa Birtaniya da martani kan haramta kungiyar Hizbullah.

Mas’ud Shajareh shugaban kungiyar kare hakkokin musulmia  Birtaniya ya bayyana cewa, babu wata doka da gwamnatin Birtaniya ta dogara da ita a cikin kundin tsarin mulkin kasar wajen haramta Hizbullah.

A bangaren babbar jami'a mai kula da harkokin siyasar wajen kungiyar tarayyar turai Federica Mogherini ta bayyana cewa; matakin da gwamnatin Birtaniya ta dauka dangane da kungiyar Hizbullah ya shafi kasar Birtaniya ne kawai, amma bai shafi kungiyar tarayyar turai ba.

A jiya ne ministan cikin gida na kasar Birtaniya Sajid Jawid ya yi da'awar cewa, kungiyar Hizbullah tana haifar tashe-tashen hankula a cikin kasashen yankin gabas ta tsakiya, ba tare da yin ishara da wata kasa guda daya da hakan ya faru ba, a kan haka ya ce sun dauki matakin haramta kungiyar tare da saka ta a cikin kungiyoyin 'yan ta'adda.

A nasa bangaren shugaban kasar Faransa Emmanuel macron ya bayyana matakin an Birtaniya da cewa ba za su amince da shi ba, domin kuwa Hizbullah tana da wakilci a cikin gwamnatin Lebanon, saboda haka babu dalilin da zai sanya a kira kungiyar ta 'yan ta'adda, kuam Faransa za ta ci gaba da mu'amala da kungiyar a hukumance.

A nata bangaren Amurka ta yaba da wannan mataki na Birtaniya, tare da bayyana cewa ya yi daidai kuma tana goyon bayan hakan.

3793604

 

 

 

captcha