IQNA

An Tarjama Kur’ani A Cikin hrshen Ashanti A Ghana

23:50 - May 03, 2019
Lambar Labari: 3483600
Bangaren kasa da kasa, an tarjama kur’ani mai tsarkia  cikin harshen Ashanti a garin Komasi da ke kasar Ghana.

Kamfanin dilalncin labaran iqna ya habarta cewa, shafin yada labarai na myjoyonline ya bayar da rahoton cewa, sheikh Harun Agikum malamin addinin muslucni a kasar Ghana, ya tarjama kur’ani mai tsarkia  cikin harshen Ashanti, wanda ya dauke shi tsawon shekaru 40.

Sheikh Abdulmumin babban limamin yankin ya bayyana wannan aiki da cewa yana da matukar muhimamnci ga dukkanin musulmin kasar.

Umar Sanda Ahmad babban limamamin sojojin kasar Ghana ya bayyana gamsuwarsa da yadda wannan aiki ya gudana a cikin nasara.

Ashanti daya ne daga cikin yarukan kasar Ghana,wanda ake magana da shia  wani bangaren kudancin kasar da kuma kasar Ivory Coast, inda kimanin muaten miliyan 2.8 ne suka magana da wannan harshe a kasar Ghana.

3808062

 

captcha