IQNA

Jiragen Yakin Saudiyya Sun Kashe Fararen Hula A Cikin Gundumar Sa'ada A Arewacin Yemen

22:57 - July 02, 2021
Lambar Labari: 3486070
Tehran (IQNA) jiragen yakin gwamnatin Saudiyya sun kaddamar da munanan hare-hare a cikin gundumar Sa'adah da ke arewacin kasar Yemen.

Tashar Almasirah ta bayar da rahoton cewa, jiragen yakin gwamnatin Saudiyya sun kaddamar da munanan hare-hare a cikin gundumar Sa'adah da ke arewacin kasar Yemen, tare da kashe fararen hula da kuma jikkata wasu.

Rahoton ya ce, baya ga hare-hare ta sama, sojojin Saudiyya sun kaddamar da wasu hare-haren da makaman atilari a kan kauyuka da suke cikin gundumar ta Sa'adah da ke kan iyaka da kasar ta Saudiyya.

Tsawon fiye da makonni biyu kenan a jere Saudiyya tana kaddamar da munanan hare-hare a kan yankuna daban-daban na kasar Yemen, lamarin da ke ci gaba da jawo salwantar rayukan fararen hula, mata da kananan yara.

Wannan na zuwa ne dai a daidai lokacin da Amurka ke da'awar cewa tana kokarin ganin an kawo karshen yaki a kan kasar Yemen, inda al'ummar kasar ta Yemen ke kallon hakan a matsayin yaudara irin da wadda gwamnatin da ta gabata a kasar ta Amurka ta rika yi kan batun yakin Yemen.

 

 

3981311

 

Abubuwan Da Ya Shafa: yaudara
captcha