Jaridar Yaum Sabi ta bayar da rahoton cewa, Hunain Ashraf Abulainain Muhammad yarinya ce mai larurar gani wadda ta hardace kur'ani mai tsarki tun tana da shekaru 7 da haihuwa a kasar Masar.
Tun bayan haihuwarta da 'yan watanni ne Hunain ta samu matsalar ciwon daji, wanda ya yi sanadiyyar har ta rasa idanunta tana da watanni 9 a duniya, amma da taimakon Allah ta samu sauki.
Tun tana karama mahaifanta suke koyar da ita karatun kur'ani, a lokacin da ta kai shekaru 7 da haihuwa ta kamala hardar kur'ani mai tsarki baki daya.
Baya ga haka kuma ta shiga gasar karatun kur'ani mai tsarki sau 20, kuma a kowace gasar ita ce take zuwa ta daya a bangaren hardar kur'ani mai tsarki.