Rahotani daga kasar Syria na cewa, an fara gudanar da tarukan arba'in na Imam Hussain (AS) a hubbaren Sayyida Zainab da ke kudancin birnin Damascus fadar mulkin kasar.
Wadannan taruka za su ci gaba da gudana har zuwa ranar arba'in na Imam Hussain (AS), inda malamai suke gabatar da jawabai kan abin da ya faru da zuriyar manzon Allah (SAW) karkashin jagorancin Imam Hussain (AS) a hannun sarakunan daular Bani Umayya, na cin zarafi da kisan gilla da tozarci.