IQNA

Ajujuwan Hardar Kur'ani A Cikin Masallatai A kasar Masar

21:10 - October 31, 2021
Lambar Labari: 3486497
Tehran (IQNA) ana shirin fara bude ajujuwan hardar kur'ani an cikin masalatai a kasar Masar.

Shafin yada labarai ya bayar da rahoton cewa, ministan harkokin addini na kasar Masar Muhammad Mukhtar Juma'a ya bayyana cewa, ana shirin fara bude ajujuwan hardar kur'ani an cikin masalatai a kasar.

Ministan na Masar ya jaddada cewa, ana shirye-shiryen gudanar da wadannan darussa da kuma gayyato amintattun malamai haddar kur'ani.
 
Da yake jawabi a wajen kaddamar da shirin da aka gudanar a Kwalejin Ilimi ta kasa da kasa, Mukhtar Juma ya ce: “A cikin masallatai za a ware wuraren koyar da yara harda Alkur’ani.
 
Ministan na Masar ya kara da cewa ana iya gudanar da wasu darussan hardar Alkur'ani a masallatai da cibiyoyin matasa ko makarantu.

 

 

4009317

 

Abubuwan Da Ya Shafa: masallatai
captcha