Ministan ma’aikatar kula da harkokin addini na Masar Mohammed Mukhtar Juma a daren jiya Lahadi 12 ga watan Disamba a wata hira ta wayar tarho da shirin "Sabuwar Masar" da aka watsa a tashar ETC, ya bayyana cewa kungiyoyin masu tsattsauran ra'ayi suna aikata laifuka karkashin tutar Musulunci da Kur'ani domin cimma burinsu.
Ya ce abin da suke yi ya yi hannun riga da koyarwar addinin musulunci, kamar yadda kuma ya yi kashedin cewa, abin suke yi yana bata sunan addinin musulunci, saboda dole ne malamai su kalubalanci irin wannan mummunar akida.
Dangane da gasar kur'ani ta duniya da ke gudana a yanzu akasar Masar kuwa, ya bayyana cewa sun kyakkyawan shiri dangane ad gasar, domin tabbatar da cewa komai ya tafi kamar yadda aka tsara.
Kamar yadda ya yi fatan alhairi ga dukkanin mahalarta wannan gasa da suka zo daga kasashe na duniya, da fatan kuma za a gudanar komai lafiya a kare lafiya.