Jakadan kasar Iran a Herat ya jajantawa iyalan wadanda harin ta'addancin ya rutsa da su a daren ranar Asabar 22 ga watan Janairu inda ya ce: Jamhuriyar Musulunci ta Iran a shirye take ta dauki wadanda suka samu munanan raunuka sakamakon wannan harin ta'addanci domin yi musu magani.
Babban jami'in jakadancin Jamhuriyar Musulunci ta Iran a birnin Herat a wata wasika da ya aike wa "Yaghoub Ali Nazari" gwamnan Khorasan Razavi ya shirya mika wadanda suka jikkata zuwa kasar Iran domin yi musu magani.
Wasikar ta bayyana cewa, da dama daga cikin wadanda harin ta'addancin na daren jiya ya rutsa da su na cikin mawuyacin hali, kuma suna bukatar kulawa cikin gaggawa a wata cibiya ta musamman a Iran.