
Abdul-Malik al-Houthi ya fada a ranar Talata yayin da yake karbar tawagogin kabilu daga sassan kasar Yemen da yaki ya daidaita, cewa "Amurka da Isra'ila na kokarin cin zarafin al'ummar musulmin duniya."
Ya kara da cewa, "Isra'ila da 'yan amshin shatanta na daukar al'ummar Yemen a matsayin makiyansu."
Al-Houthi dai yana magana ne a kan kasashen Larabawa yankin da suka shiga yarjejeniyar daidaitawa da gwamnatin Isra'ila da Amurka ke marawa baya, kuma tun a wancan lokaci suke kokarin mika kansu ga gwamnatin mamaya ta hanyar daidaita alaka da ita.