Kamfanin dillancin labaran AFP ya bayar da rahoton cewa, jami'an Taliban sun sanar da cewa an bude jami'o'in gwamnati ga 'yan mata a larduna shida na Laghman, Nangarhar, Kandahar, Nimroz, Helmand da Farah a ranar Laraba.
Dangane da shigar da 'yan mata a jami'o'in gwamnatinTaliban wasu dalibai mata kadan ne suka halarci azuzuwan da aka ware ta hanyar raba jinsi.
Hakkokin mata musamman a fannin ilimi na daya daga cikin batutuwan da suka fi daukar hankali tsakanin gwamnatin Taliban da kasashen duniya.
Duk da sake bude makarantun firamare a Afganistan, makarantun sakandare da jami'o'in gwamnati a galibin lardunan kasar sun kasance a rufe ga 'yan mata tun bayan da 'yan Taliban suka karbe mulki tare da janye sojojin Amurka a watan Agustan da ya gabata.
https://iqna.ir/fa/news/4033359