IQNA

20:53 - February 08, 2022
Lambar Labari: 3486925

Kwamitin Kula Da Fursunoni Falastinawa Da Ke Hannun Isra'ila Ya Koka Kan Mawuyacin Halin Da Fursunonin Suke Ciki

Tehran (IQNA) Kwamitin Falastinawa da ke kula fursunonin Falastinawa da Isra'ila ke tsare da su ya koka kan mawuyacin halin da fursunonin suke ciki.

Kwamitin Kula Da Fursunoni Falastinawa Da Ke Hannun Isra'ila Ya Koka Kan Mawuyacin Halin Da Fursunonin Suke Ciki

A cikin wani bayani da ya fitar a yau, Kwamitin Falastinawa da ke kula da fursunonin Falastinawa da Isra'ila ke tsare da su ya koka kan mawuyacin halin da fursunonin suke ciki.

A wani rahoton kuma kamfanin dillancin labaran Wafa na Falasdinu ya rawaito cewa sojojin Isra'ila sun kashe wasu Falastinawa uku a yau lamarin ya faru ne a unguwar al-Makhfeya da ke birnin na Nablus.

Rahoton ya kara da cewa, shafin sadarwa na yanar gizo na hukumar Falastinawa ya ce, dakarun na musamman na Isra’ila sun kai hari a unguwar ne da wata motar farar hula dauke da lambar Falasdinu.

Daga nan ne sojojin suka fara bude wuta kan wata motar da ke tafiya a kusa da wajen, inda suka kashe uku daga cikin mutanen da ke cikinta tare da kame na hudu.

Dakarun Al-Aqsa Martyrs Brigade sun bayyana wadanda abin ya shafa a matsayin mambobin kungiyar gwagwarmayar da ke Yammacin Kogin Jordan, inda ta bayyana sunayensu da Ibrahim al-Nablusi, Adham Mabrouk, da Muhammed al-Dakhil.

 

4034468

 

 

 

 

captcha