IQNA

Rumfar Cibiyar Hubbaren Imam Hussain A Baje Kolin Kur’ani na Kasa Da Kasa

17:12 - April 19, 2022
Lambar Labari: 3487191
Tehran (IQNA) Rumfar Cibiyar Hubbaren Imam Hussain da ke kula da ayyukan kur'ani mai tsarki ita ce rumfa daya tilo daga kasashen waje a bikin baje kolin kur'ani na kasa da kasa karo na 29, wanda aka baje kolin fastoci na ayyukan kur'ani daban-daban.

Kamfanin dillancin labaran iqna ya habarta cewa, ya nakalto daga shafin sadarwa na yanar gizo na iqna cewa, sakamakon bullar cutar corona da kuma matsalolin kiwon lafiya, kasashen ketare ba su halarci taron baje kolin kur’ani na kasa da kasa karo na 29 a wannan shekara kai tsaye ba, kuma rumfar ayyukan kur’ani ta Rumfar Cibiyar Hubbaren Imam Hussain ita ce rumfar da aka kafa a babban dakin baje kolin.

Rukunin  ya kunshi bangarori daban-daban inda aka rika baje kolin fastoci na ayyukan cibiyar yada ayyukan alkur'ani ta kasa da kasa da kuma Darul kur'ani, wadanda dukkaninsu ke da alaka da Hubbaren Imam Hussain (AS).

Sayyid Qasim Al-Batat shugaban rumfar ya shaidawa kamfanin dillancin labaran iqna cewa: A bangaren ayyuka na cibiyar yada kur'ani ta kasa da kasa, allunan ayyukan cibiyar sun hada da darussa na horar da malaman kur'ani a kasar Indonesia, da'irar kur'ani a Pakistan, da kuma baje kolin kur'ani na kasa da kasa a Al-Harmain."

Ya kara da cewa wani dutsen marmar da ke cikin harabar hubbaren Husaini da babbar tuta na hubbaren Imam Husaini (AS) na daga cikin ayyukan da aka gabatar a wannan rumfar da kuma gudanar da taron karawa juna sani a wajen rufe taron baje kolin kur'ani na duniya.

آستان حسینی؛ تنها غرفه خارجی حاضر در نمایشگاه بین‌المللی قرآن

آستان حسینی؛ تنها غرفه خارجی حاضر در نمایشگاه بین‌المللی قرآن

آستان حسینی؛ تنها غرفه خارجی حاضر در نمایشگاه بین‌المللی قرآن

 

 

https://iqna.ir/fa/news/4050624

 

captcha