IQNA

15:53 - August 21, 2022
Lambar Labari: 3487722

Ofishin Jakadancin Bangladesh ya karrama makarancin kur'ani dan kasar Masar

Tehran (IQNA) Jakadan kasar a Masar ya karrama "Osameh El-Baili Faraj" makaranci dan kasar Masar yayin wani biki a ofishin jakadancin Bangladesh dake birnin Alkahira.

Ofishin Jakadancin Bangladesh ya karrama makarancin kur'ani dan kasar Masar

Kamfanin dillancin labaran kur’ani na iqna ya habarta cewa, ya nakalto daga shafin sadarwa na yanar gizo na Siddi Al-Balad cewa, Osama Al-Baili Faraj wanda ya yi nasarar zama na daya a gasar kur’ani ta kasa da kasa ta ofishin jakadancin Bangladesh da ke birnin Alkahira, ya samu karramawa a lokacin wani biki da “Mohammed Munir-ul-Islam” Jakadan Bangladesh a Alkahira ya jagoranta.

Osama Faraj yana daya daga cikin mazauna birnin "Bila" da ke lardin "Kafr al-Sheikh" na kasar Masar kuma daya ne daga cikin fitattun ma'abota karatu a wannan zamani na kasar kuma yana da murya mai dadin karantawa.

Ya taso a gidan Al-Qur'ani kuma yana dan shekara 11 ya zama mai haddar Al-Qur'ani tare da samun fa'idar kasancewar malaman Al-Qur'ani da shehunai da Sayyidi "Abdul Wahab Jad" baffansa.

Muhammad Seyyed Tantawi, Abdul Fattah Tarouti, Sheikh Qutb al-Tawil, Sheikh "Ahmed Awad Abu Fayuz" na daga cikin malaman wannan makarancin na Masar.

Usama Faraj a tattaunawarsa da Siddi al-Balad ya yi nasiha ga masu haddace mafari da masu sha’awar kur’ani inda ya ce: “Wasu abubuwa suna da matukar muhimmanci a tafarkin haddar Alkur’ani, kuma ya kamata masu haddar su sani. daya daga cikin wadannan abubuwa shi ne karanta littafin Allah da kyau da kiyaye shi gaba daya.

4079569

 

 

captcha