Tehran (IQNA) Babban birnin kasar Guinea an gudanar da wani gagarumin biki na karrama malaman kur'ani na kasar su 190.

Kamfanin dillancin labaran kur’ani na iqna ya habarta cewa, ya nakalto daga shafin sadarwa na yanar gizo na Baladi cewa, an gudanar da wannan gagarumin biki ne a filin wasa na Lansana Conte, inda aka karrama mahardatan kur’ani mai tsarki 190, 23 daga cikinsu mata ne.
Matan da suka haddace kur'ani a wannan bikin sun fito ne daga cibiyoyin Darul-Salam, Othman bin Affan da kuma Noor al-Qur'an. An gudanar da bikin ne karkashin jagorancin Dansa Khroma, shugaban majalisar rikon kwarya ta kasa, da dimbin jami'an gwamnati, jami'an diflomasiyya na kasashen waje da kuma dimbin 'yan kasar.




