Kamfanin dillancin labaran iqna ya habarta cewa, kungiyar Islamic Society of Markham (ISM) ta sanar a cikin wata sanarwa cewa, a ranar Alhamis 17 ga watan Afrilu, wani mutum ya shiga masallacin Markham da ke da tazarar kilomita 30 daga arewacin birnin Toronto, kuma da alama ya yaga Alkur’ani sannan ya zagi masu ibada.
"Na yi matukar bakin ciki da jin wannan mummunan laifin nuna kyama da nuna wariyar launin fata ga al'ummar musulmin Markham," in ji Neg a wani sako da ta wallafa a shafin Twitter.
Sai dai ba ta fadi cikakken bayani kan lamarin ba amma ta ce: Wannan tashin hankali da kyamar Musulunci ba su da gurbi a cikin al'ummominmu.
Musulmi suna daukar duk wani yunkuri na cutar da Alkur’ani a matsayin abin da ba a so ba saboda sun dauki littafin Musulunci a matsayin maganar Allah. Wannan lamari dai ya faru ne a cikin watan Ramadan lokacin da masu ibada ke zuwa masallatai.
A cewar jami'an kungiyar Islama ta Markham, dubban mutane ne ke halartar bukukuwan addini a masallacin Markham.
Majalisar musulmin kasar Canada ta bayyana a wani sako da ta wallafa a shafinta na Twitter cewa ta damu matuka da lamarin.