IQNA - A safiyar yau ne Jagoran juyin juya halin Musulunci Ayatullah Sayyid Ali Khamenei ya ziyarci wurin baje kolin littafai na kasa da kasa karo na 35 a birnin Tehran a lokacin da yake halartar Maslacin Imam Khumaini (RA).

Kamfanin dillancin labaran kur’ani na iqna ya habarta cewa, ya nakalto daga shafin sadarwa na yanar gizo na ofishin jagora cewa, a safiyar yau litini 13 ga watan Mayu ne a ci gaba da gudanar da taron baje kolin littafai na kasa da kasa na birnin Tehran karo na 35, jagoran juyin juya hali ya samu halartar wurin a masallacin Imam Khumaini (R.A)