IQNA

Karim Mansouri makarancin kur’ani na kasa da kasa ya karanta wasu ayoyin Kur’ani

15:44 - May 25, 2024
Lambar Labari: 3491215
IQNA - A ciki gaban taron makokin shahidan hidima, Bayan haka Mahmoud Karimi mai yabon Ahlul Baiti (a.s) da zazzafan muryarsa ya gabatar da jinjina ga shahidai a kan hanyar hidima.

Daga nan sai karatun ayoyin kur’ani tare da Ghasem Moghadami, makarancin kasa da kasa na kasar Iran

An ci gaba da gudanar da taron  tare da karatun Raudah tare da  Morteza Taheri, babban malamin Ahlul Baiti (AS) a wajen zaman makokin Ayatullah Raisi da tawagarsa.

Hamidreza Ahmadiwafa, makarancin kasa da kasa na kasar Iran ya karanta ayoyi a cikin suratul Rahman.

Bayan haka, Hojjat al-Islam Nasser Rafiei, farfesa na Jami’a da Hauza, ya gabatar da jawabi.

Ya yi nuni da abin da ke cikin ziyarar hajjin Aminullah ya ce: Ya Allah mun amince da duk abin da ka tsara  da hukuncinka, kuma mun natsu.

Jagoran juyin juya hali ya ce, mun rasa manyan jiga-jigai, amma kuma ba za mu ja da kaddara ta Allah ba, muna kuka amma ba korafi ba, Domin kuwa Abin da ya faru na ibtila’i ga Manzon Allah (SAW) ba a taba jarabtar wani dan adam da shi ba, domin shi ne mafi daraja da daukakar matsayi a wajen Allah, a kan haka jarabawarsa tafi ta kowa, kuma da shi muke koyi  wajen jurewa jarabawa da ubangiji, domin manzon Allah shi ne babban abin koyi ga dukkanin masu imani.

 

 
 
 
 
 

 

 

 

 

 

 

captcha