IQNA

16:34 - October 06, 2024
Lambar Labari: 3491990

Fafaroma ya jaddada muhimmancin samar da zaman lafiya a yammacin Asiya

IQNA - Shugaban mabiya darikar Katolika na duniya, yayin da yake jaddada wajabcin samar da zaman lafiya a yammacin Asiya, ya bayyana cewa ba zai iya yin shiru ba dangane da rikicin kasar Lebanon.

Fafaroma ya jaddada muhimmancin samar da zaman lafiya a yammacin Asiya

Kamfanin dillancin labaran reuters ya nakalto shugaban mabiya darikar katolika na duniya ya mayar da martani dangane da ci gaba da aikata laifukan gwamnatin sahyoniyawan a kasar Labanon.

A jiya Asabar fadar Vatican ta nakalto Paparoma Francis shugaban mabiya darikar Katolika na duniya yana cewa Paparoma yana goyon bayan samar da zaman lafiya a yammacin Asiya.

A cewar Fafaroma Francis, fadar Vatican ba za ta iya yin shiru ba dangane da irin wahalhalun da bil'adama ke fuskanta a Lebanon.

A makon da ya gabata ne shugaban mabiya darikar Katolika na duniya ya yi kira da a tsagaita bude wuta cikin gaggawa a kasashen Lebanon, Gaza da sauran yankunan Falasdinu da ke mamaye da su, a daidai lokacin da gwamnatin sahyoniyawan ke ci gaba da kai hare-hare kan kasar Labanon.

A karshen ziyararsa a Belgium Paparoma Francis ya ce: Ina rokon dukkanin bangarorin da su gaggauta tsagaita wuta a kasar Lebanon, Gaza da sauran Falasdinu.

Jagoran mabiya darikar Katolika na duniya ya kara da cewa: Labanon sako ne, amma a halin da ake ciki yanzu sako ne da ake tarwatsa shi. Wannan yakin ya yi babbar illa ga mutane; Mutane da yawa suna mutuwa kowace rana a Gabas ta Tsakiya.

 

 

4240762

 

 

captcha