IQNA

Fafaroma ya jaddada muhimmancin samar da zaman lafiya a yammacin Asiya

16:34 - October 06, 2024
Lambar Labari: 3491990
IQNA - Shugaban mabiya darikar Katolika na duniya, yayin da yake jaddada wajabcin samar da zaman lafiya a yammacin Asiya, ya bayyana cewa ba zai iya yin shiru ba dangane da rikicin kasar Lebanon.

Kamfanin dillancin labaran reuters ya nakalto shugaban mabiya darikar katolika na duniya ya mayar da martani dangane da ci gaba da aikata laifukan gwamnatin sahyoniyawan a kasar Labanon.

A jiya Asabar fadar Vatican ta nakalto Paparoma Francis shugaban mabiya darikar Katolika na duniya yana cewa Paparoma yana goyon bayan samar da zaman lafiya a yammacin Asiya.

A cewar Fafaroma Francis, fadar Vatican ba za ta iya yin shiru ba dangane da irin wahalhalun da bil'adama ke fuskanta a Lebanon.

A makon da ya gabata ne shugaban mabiya darikar Katolika na duniya ya yi kira da a tsagaita bude wuta cikin gaggawa a kasashen Lebanon, Gaza da sauran yankunan Falasdinu da ke mamaye da su, a daidai lokacin da gwamnatin sahyoniyawan ke ci gaba da kai hare-hare kan kasar Labanon.

A karshen ziyararsa a Belgium Paparoma Francis ya ce: Ina rokon dukkanin bangarorin da su gaggauta tsagaita wuta a kasar Lebanon, Gaza da sauran Falasdinu.

Jagoran mabiya darikar Katolika na duniya ya kara da cewa: Labanon sako ne, amma a halin da ake ciki yanzu sako ne da ake tarwatsa shi. Wannan yakin ya yi babbar illa ga mutane; Mutane da yawa suna mutuwa kowace rana a Gabas ta Tsakiya.

 

 

4240762

 

 

captcha