Shafin yanar gizo na kasar Libya habarta cewa, an gudanar da wannan karatun kur’ani ne a karamar hukumar Jufra, kuma an kammala shi a ranar Juma’a 10 ga watan Janairun 2024.
Malamai maza da mata 120 daga dukkan kungiyoyin Ahlus Sunna daga cibiyoyin haddar kur’ani na kasar Libya ne suka halarci wannan horon wanda ya dauki tsawon kwanaki hudu ana yi.
haddar Suratul Hamd, Ayat al-Kursi, da ayoyin karshe na surar Baqarah na daga cikin shirye-shiryen wannan darasi, kuma an samu saukin tafsirin kur'ani ga mahalarta taron.
Sauran shirye-shirye na wannan darasi sun hada da gyara karatun da kuma bayyana hadisan ma'aiki akan maudu'in koyon ilimi da shiga cikin da'irar ilimi.
Libya kasa ce a Arewacin Afirka da ke kudu da tekun Bahar Rum. Kimanin kashi 97 cikin 100 na mutanen Libya suna bin addinin Musulunci, galibinsu 'yan Sunna. Haka kuma wasu tsirarun musulmin Ibadi suna zaune a kasar Libya.