
Shafin Al-Ahram News ya bayar da rahoton cewa, Ahmed Al-Tayeb ya karbi bakuncin wasu dalibai ‘yan kasashen waje da suka shiga makarantar haddar Alkur’ani mai girma ta Imam Al-Tayeb da ke hedikwatar cibiyar Islama ta Al-Azhar da ke birnin Alkahira a ranar Laraba 1 ga watan Disamba, 2019.
A yayin taron, Ahmed Al-Tayeb ya saurari fitattun daliban karatun kur’ani mai tsarki tare da karatun kur’ani guda goma tare da yaba wa bajintar karatun kur’ani mai tsarki, wanda ke nuni da irin namijin kokarin da jami’ai da malaman makarantar suka yi.
A bangare guda kuma daliban sun jaddada cewa makarantar haddar kur’ani mai tsarki ta Imam Al-Tayeb ta saukaka musu kwarewar haddar kur’ani.
A karshen taron, Shehin Malamin na Azhar ya shawarci daliban da su ci gaba da kokarinsu na kara fahimtar ma'anoni da tafsirin kur'ani mai girma, da kuma rashin gamsuwa da haddar ayoyin kur'ani mai girma, ta yadda nan gaba kadan za su zama jakadun Azhar a kasashensu. Ya kuma jaddada cewa kungiyar Azhar ba za ta yi kasa a gwiwa ba wajen ba su wani tallafi.