
A cewar Ma'an, sakatariyar kungiyar hadin kan kasashen Larabawa ta sanar da matakin da kungiyar ta dauka na gudanar da wani taro na musamman a yau Lahadi, dangane da matakin da gwamnatin Sahayoniya ta dauka na amincewa da kasar Somaliland mai cike da cece-kuce.
Kwamitin Sulhu ya kuma sanar da cewa zai gudanar da taro a gobe litinin, domin duba matakin da gwamnatin sahyoniyawan ta dauka bisa bukatar Somaliya.
Sanarwar amincewar da gwamnatin Sahayoniya ta yi wa Somaliland ya biyo bayan tofin Allah tsine daga kasashen yankin, Larabawa, Musulunci da kuma na duniya baki daya.
Kungiyar hadin kan kasashen musulmi da kasashen Larabawa da na kasashen musulmi 21 sun fitar da wata sanarwa, inda suka yi watsi da kakkausar murya kan sanarwar amincewa da gwamnatin Sahayoniya ta yi wa Somaliland, suna mai cewa matakin wani sabon abu ne mai hadari da kuma barazana ga zaman lafiya da tsaro a duniya.
An bayyana hakan ne a cikin wata sanarwar hadin gwiwa da kungiyar da ministocin harkokin wajen kasashen Iran, Turkiya, Jordan, Masar, Aljeriya, Comoros, Djibouti, Gambia, Iraq, Kuwait, Libya, Maldives, Nigeria, Oman, Pakistan, Palestine, Qatar, Saudi Arabia, Somalia, Sudan da Yemen suka fitar, wanda ma'aikatar harkokin wajen kasar Jordan akan Platform X ta buga.
Sanarwar ta sake jaddada kin amincewa da sanarwar da Isra'ila ta yi na amincewa da yankin Somaliland da ke cikin Tarayyar Somaliya, "idan aka yi la'akari da mummunan sakamakon wannan mataki da ba a taba ganin irinsa ba kan zaman lafiya da tsaro a yankin kahon Afirka da kuma yankin tekun Bahar Maliya, da kuma mummunan tasirinsa ga zaman lafiya da tsaro na kasa da kasa, wanda kuma ke nuni da irin yadda Isra'ila ke nuna kyama da rashin mutunta dokokin kasa da kasa."
Sanarwar ta yi nuni da cewa amincewa da 'yancin kan wasu sassan kasar ya kafa tarihi mai hatsari da kuma yin barazana ga zaman lafiya da tsaro na kasa da kasa, da kuma ka'idojin dokokin kasa da kasa da na Majalisar Dinkin Duniya.