IQNA

Za A Girmama Makaranta Kur'ani Da Maharda A Masar A ranar Idil Fitr

17:59 - July 23, 2014
Lambar Labari: 1432780
Bangaren kasa da kasa, za a girmama makaranta da mahardata kur'ani main a kasar a ranar idin karamar salla mai zuwa da nufin kara karfafa gwiwarsu wajen ci gaba da bayar da kwazo.

 Kamfanin dilalncin labaran Iqna ya habarta cewa, ya nakalto daga shafin sadarwa na yanar gizo na Al-yaum Sabi cewa, ana shirin girmama makaranta da mahardata kur'ani main a kasar a ranar idin karamar salla mai zuwa da nufin kara karfafa gwiwarsu wajen ci gaba da bayar da kwazo a karatunsu da kuma harda. A wani labarin na daban an kashe wani jami’in sojan kasar Masar guda a yankin Sina. Tashar telbijin din Presstv ta nakalto majiyar tsaron kasar Masar na fadin cewa an kashe sojan ne a lokacin da ya ke kan hanyarsa ta komawa gida daga wurin aiki a garin al-Arish da ke gundumar Sina. Majiyar tsaron masar ta ce maharan sun gudu bayan da su ka kashe sojan, sai dai an baza koma domin kamo su. A ranar talatar da ta gabata mai dai majiyar sojan Masar ta sanar da samun nasarar rusa wasu sansanoni ‘yan ta’adda a cikin yankin Sina tare kuma da kashe bakwai daga cikinsu. 1431907

Abubuwan Da Ya Shafa: masar
captcha