Kamfanin dillancin labaran ikna ya nakalto daga shafin internet na (MUHIT) cewa; an fara gudanar da taron ne tsakanin Azhar da Vatican ya a birnin Rom, da nufin kara karfa fahimtar juna tsakanin mabiya addinan kiristanci da musulunc. Wanda ya jagoranci tawagar Azhar zuwa birnin na Rom (Ali Abdulbaki) ya bayyana cewa; wajibi ga dukkanin bangarorin biyu wato musulmi da kirista da su karfafa fahimtar juna tsakaninsu, kasantuwar addinansu addinai ne da aka safkar daga sama, dole ne a samara da fahimtar juna mai dorewa tsakanin bangarorin biyu, wanda kuma hakan nauyi ne day a rataya kan jagororin addinan biyu.
368966