Kamfanin dillancin labaran iqna ya habarta cewa, a wani rahoto day a nakalto daga shafin sadarwa na internet na kafil an bayyana cewa, Ana ci gaba da gudanar da gyaran hasumiyoyin hubbaren Abul Fadl Abbas a birnin Karbala mai alfarma da ke kasar Iraki, wanda za a kammala a a cikin watan Sha'aban mai zuwa. Bayanin ya ci gaba da cewa yanzu haka dai aiki ya mika kuma za a gudanar da taron kammala aikin tare da halartar manyan mutane na cikin kasar da wajenta a nan da karshen watan sha'aban. 595690