Bangaren kasa da kasa: a birnin Doha babban birnin kasar Katar za a nuna tsaffin rubutun kur'ani lamarin da zai kayatar da wadanda za su halarci gurin kuma za a gudanar da wannan baje kolin ne a ranekun sha hudu da kuma sha biyar ga watan Isfand na shekara ta dubu daya da dari uku da tamanin da tara hijira shamsiya a birnin Doha fadar mulkin kasar Katar.
Kamfanin dillancin labarai na Ikna da ke kula da harkokin kur'ani a nan jamhuriyar musulunci ta Iran Ikna ne ya watsa rahoton cewa; a birnin Doha babban birnin kasar Katar za a nuna tsaffin rubutun kur'ani lamarin da zai kayatar da wadanda za su halarci gurin kuma za a gudanar da wannan baje kolin ne a ranekun sha hudu da kuma sha biyar ga watan Isfand na shekara ta dubu daya da dari uku da tamanin da tara hijira shamsiya a birnin Doha fadar mulkin kasar Katar. A gurin za a tara masana fasaha na duniya wadanda za su nuna kwarewa da kuma iya a gurin da kuma baje kolin abubuwan da suka nakalta ta fuskar fasaha.
752621