Kamfanin dillancin labarai na ikna da ke kula da harkokin kur'ani mai girma a nan jamhuriyar musulunci ta Iran ne ya watsa rahoton cewa; al'ummar kasar Karkazistan sun karbi da halaratr taron koyar da kur'ani mai girma da hannu biyu da aka gudanar a masallacin Duba daya daga cikin manyan masallatai a masu girma a birnin Bishkak fadar mulkin kasar .Wannan zaman karatun kur'ani mai girma za a ci gaba da gudanarwa har zuwa farkon watan Khurdad na shekara ta dubbu daya da dari uku da tis'in hijira shamsiya da ya yi daidai da watan rajab . Kuma wannan zaman karatun kur'ani mai girma za a rika gudanarwa a kowa ne ranekun litin da laraba na kowa ne mako bayan sallar magriba da kuma Abdallah bin Mas'ud da shekh Nur Muhammad da suke daga cikin malaman Hauza ta birnin kuma za su rika hadawa da tafsirin kur'ani mai girma kuma matasa da dama suka amsa wannan taro na yada ilimin kur'ani mai girma.
933350