Kamfanin dilalncin labaran iqna ya habarat cewa ya nakalto daga shafin sadarwa na World Bulletin cewa, rahoton tawagar MDD da ta isa yankin ta bukaci da a kawo karshen killacewar da ake yi da kuma gina matsugunnai,
Ya kira taron menema labarai inda ya bukaci magabatan haramcecciyar kasar Isra’ila da suka kawo karshen killacewar da suka yi wa yankin ya ce hakki ne a kan kungiyoyin kasa da kasa da su gina zirin bayan rusu gidaje dubu 11 tare da neman da kadda ta hana shigar kayayyakin gini gami da ababen bukatuwa na al’ummar yankin.
Tun a shekarar dubu biyu da bakwai ne magabatan Isaraila suka killace yankin na zirin, lamarin da ya yi sanadiyar jefa al’ummar yankin cikin mawuyacin hali na kuncin rayuwa,talauci da rashin aikin yi ga mafi yawan matasan yankin, alkaluma na cewa yankin na zirin za mai yawan al’umma da adadinsu ya haura zuwa million daya da dubu 17 sun shiga cikin wani mawuyacin hali a tsahon shekaru bakawai a suke cikin kurkurun Isra’ila.
A shekarar da ta gabata Haramcecciyar kasar isra’ila ta kaiwa Al’ummar zirin hari ta kasa da ta sama a karo na uku cikin shekaru da suka gabata, lamarin da ya jefa Al’ummar yankin cikin mawuyacin hali, a cikin wannan yaki na kwanaki hamsin, kimanin Palastinawa 132 gami da wasu fiye dubu biyu da dari biyu suka yi shahada daga ciki a kwai kananen yara dri biyar da sabain da bakwai.
laifuka ta duniya ke cewa a kwai yiyuwar hukunta manya jami’an tsaron HKI a gaban kotun saboda laifin yakin da suka yi a zirin.
3360459