IQNA

Tattaunawa A Tsakanin Addinai A Nahiyar Afirka Ya Zama Wajibi

23:43 - November 26, 2015
Lambar Labari: 3457371
Bangaren kasa da kasa, jagoran majami’ar Catholic ya bayyana a lokacin da yake zantawa da shugabannin addinai a kasar Kenya ya bayyana cewa ya zama wajibi a gudanar da tattaunawa a tsakanin addinai.


Kamfanin dillancin labaran Iqna ya habarta cewa, ya nakalto daga shafin sadarwa na yanar gizo na Reuters Arabic cewa, Pop Francis a lokacin da yake ganawa da jagororin addinai 25 yau a birnin Nairobi na kasar Kenya ya bayyana cewa, an ayin amfani da sunan addini ne wajen ruda matasa da kuma saka tattauran da kan kai su ga ta’addanci.

Francis y ace batun tattanawa a tsakanin mabiya addinai a nahiyar Afirka ba abu ne na zabi ba, wajibi ne yin hakan.

Ya ce babu yadda za a yi a kare ayyukan ta’addanci da sunan ubangiji.

A nasa bangaren Abdulgafir Bu Sa’idi shugaban majalisar mabiya addinin muslunci a kasar ta kenya ya bayyana cewa, kasantuwarmu muna Imani da ubangiji guda daya, kuma muna rayuwa  adunbiya daya, dole ne mu karbi juna mu zauna lafiya.

Abin tuni a nan shi ne bayan kasar Kenya, Pop zai kama hanaya zuwa kasar Uganda inda zai gana da yan kasar Afirka ta tsakiya da ke fama da tashin hankali.

3457317

Abubuwan Da Ya Shafa: Africa
captcha