
Kamfanin
dillancin labaran iqna ya nakalto daga shafin sadarwa na yanar gizo na jaridar
Yaum sabi cewa, taron na Davos dai za a bude shi gobe Laraba tare da halartar
shugabannin wasu kasashe da kuma fitattun mutane daga kasashe kimanin 150 na
duniya, inda Shauki Allam zai gabatr da jawabi ga taron.
Shauki Allam
zai yi bayani kan matsayin addinin mulsunci wajen kira zuwa ga zaman lafiya da
fahimtar juna tsakaninsa da sauran addinai, da kuma yadda muslunci yake kin
ayyuka na tashin hankali.
Haka nan
kuma daga cikin muhimamn lamurran da jawabin nasa zai mayar da hankalia kansu akwai batun yadda ayyukan ta’addanci
suka bata sunan addinin muslunci a duniya, da kuma yadda ya zama wajibi a
banbance tsakanin muslunci na gaskiya da kuma ta’addanci.
Shauki Allam
kafin barin kasar Masar ya bayyana cewa; wannan taron na Davos babbar dam ace ga
musulmi da su bayyana addininsu da kuma koyarwasa ga dunya, maimakon barrin
wasu suna Magana da yawun muslunci suna bata masa suna a duniya.
Malamin na
Masar zai gana da babban sakararen majalisar dinkin duniya akasar ta
Switzerland Banki Moon, kamar yadda kuma zai gana da wasu daga cikin manyan
jami’ai da ska shirya taron, gami da jagoran majami’ar Angalican ta kasar
Birtaniya.