IQNA

Malam Sudan Sun Bukaci A Janye Dokar Hana Wa'azi A Kasar

23:53 - August 25, 2016
Lambar Labari: 3480743
Bangaren kasa da kasa, majalisar malaman addinin muslunci ta kasar Sudan ta bukaci da a janye dokar hana yin duk wata Magana ta addini ba da izinin gwamnati ba.
Kamfanin dillancin labaran iqna ya habarta cewa, ya nakalto daga shafin jaridar Al-dastur cewa, Muhammad Usman Saleh shugaban majalisar malaman addinin musulunci ta kasar Sudan ya bayyana a gaban manema labarai cewa, suna bukatar a janye dokar hana maganar addini a kasar.

Ya ce kafa wannan doka zai takura malaman addini da sauran masana, alhali kasar Sudan kasa ce ta musulmi wadanda suke bukatar fadakarwa akowane lokaci, kuma mutane suna da masaniya kan addini, a duk lokacin da wani ya kauce a maganar addini a na take za su gane.

A kan haka malamin y ace majalisar tasu tana mika kira ga mahukuntan kasar da su janye wannan doka, amma kuma za a iya saka wasu hanyoyi na tantance abin abi da mutane uke fada, domin tabbatar da cewa ba a yada wai abu da ya kauce ma koyarwar muslucni ba, amma ba hana Magana kan addini ba baki daya sai da izinin gwamnati.

Babbar manufar gwamnatin Suda ta kafa wannan doka dai ita ce hana yaduwar kidar ta'addaci, wadda masu dauke da akidar kan yi amfani da hanoyin wa'zi wajen cusa wannan mummunar akida ta kafirta musulmia cikin zukatan matasa musamman, wanda hakan daga bisani ya kan kai matasa zuwa ga shiga ta'addanci da sunan addini.

3524813
Abubuwan Da Ya Shafa: iqna sudan
captcha