Kamfanin dillancin labaran kur’ani
na iqna ya habarta cewa ya nakalto daga shafin sadarwa na yanar gizo na tashar
alalam cewa, Ahmad Tahir shugaban kwamitin kula da tarukan ashura a lardin
Diyala ya bayyana cewa, akwai tawagogi 670 ‘yan sunna suna sahun gaba wajen
shirya tarukan ashura a lardin inda tawaga 40 daga cikin nasu ne.
Ya ce ko shakka babu a wannan karon an samu gagarumin canji a tarukan da ake gudanarwa a Iraki na ashura, inda lamarin bai takaitu da yan shi’a ba, yan sunna da dama sun shiga cikin lamarin ana yi tare da su.
Ahmad tahir ya ce yan sunna a Iraki sun yi imanin cewa, lamarin Imam Hussain (AS) lamari ne na dkkanin musulmi bay an shi’a kadai ba, saboda haka ba a bar su a bay aba wajen raya wannan taro mai albarka na tunawa da shahadar jikan manzon Allah da iyalan gidan manzo.