IQNA

Taron Kara wa Juna Sani Kan Musulunci A Kasar Jamus

20:34 - November 12, 2016
Lambar Labari: 3480932
Bangaren kasa da kasa, an fara gudana r da wani zaman taro na karawa juna sani kan addinin muslunci a jami'ar Haidelburg da ke kasar Jamus.
Kamfanin dillancin labaran kur'ani na iqna ya habarta cewa ya nakalto daga shafin sadarwa na yanar gizo na cibiyar yada al'adun musulunci ta Iran cewa an shirya taron ne a matsayin wata hanya ta yin bayani kan muslunci ga wadanda ba musulmi musamman ma dai mabiya addinin kirista.

Bayanin ya ce taron yana samun halartar masana daga dukkanin bangarori biyu na musulmi da ma wadanda ba musulmi ba, musamman ma dai mabiya addinin kirista, wadanda suke da bukatar sani abu kan muslunci.

Babbar manufar taron dai wanda ba shi ne karo na farko ba, ita ce fito da hakikanin fuskar muslunci ga wadanda ba musulmi ba, domin kuwa bata sunan muslunci ya yi tasiri matuka musamman ma a cikin kasashen yammacin turai kan batun ta'addanci.

An gabatar da laccoci kan matsayin muslunci dangane da zamantakewa da kuma siyasa gami da akidar sauran addini da ma yadda muslunci yake kallon dan adam baki daya, wanda kaida a muslunci ita ce Allah ya aiko manzonsa mai tsira da amincin Alllah da iyalansa tasrakaka a matsayin rahma ne ga bil adama baki daya.

Su a nasu bangaren wadanda suka halarci taron daga bangaren mabiya wasu addinai sun gabatar da jawabansu da kuma yin tambayoyi kan abin da ya shige musu kan muslunci kuma an ba su amsoshi daidai da tambayoyin nasu.

Kiamnin shekaru 7 kenan ana gudanar da wannan taro wanda yake a kowace shekara yake kara bunkasa.

3545316


captcha