IQNA

23:06 - February 28, 2017
Lambar Labari: 3481270

Masarautar Bahrain ta Kame Kananan Yara 6

Bangaren kasa da kasa, masarautar Bahrain ta ta kame fararen hula 17 da suka hada da kanann yara a cikin wannan mako.

Masarautar Bahrain ta Kame Kananan Yara 6

Kamfanin dillancin labaran IQNA ya nakalto daga tashar alalam cewa, masarautar mulkin kama karya ta kasar Bahrain ta kame fararen hula 17 da suka hada da kananan yara 6 a cikin makon da ya gabata, amma daya daga cikinsu ne kawai ta saka.

Hakla na kumarahoton ya kara da cewa masarautar ta yanke hukunci a kan wasu fararen hla 19 a cikin wannan mako bisa dalilai na siyasa, 8 daga cikinsu kuma ta janye musu izinin zama ‘yan kasar.

A cikin wannan makon an gudanar da jerin gwano a yankuna 129 a kasar, jami’an tsaron gidan sarautar kasar sun yi amfani da hayaki mai sanya hawaye da kuma duka da kulake domin tarwatsa masu zanga-zangar a wasu yankunan.

3579158


captcha