IQNA

Jaddada Muhimamncin Gudanar Da Ayyukan Ilimi A Masallatai A Kenya

23:19 - April 13, 2017
Lambar Labari: 3481402
Bangaren kasa da kasa, mataimakin babban limamin Juma’a na birnin Nairobi a kasar Kenya ya jaddada muhimamncin gudanar da ayyuka na ilimi a cikin masallatai.

Kamfanin dillancin labaran iqna ya bayar da rahoton cewa, a wani taron karawa juna sani da ya gudana a yau a birnin Nairobi na kasar Kenya, mataimakin limamanin Juma’a na Nairobi ya bayyana muhimmanci ci gaba da wayar da kan jama’a a masallatai.

Sheikh Juma’a Amir shi ne mataimakin babban limamain masallacin Juma’a na birnin Nairobi, ya bayyana wannan taron karawa juna sani wanda ya kunshi malamai da limamai na kasar Kenya cewa, masallaci ba wurin salla ne ba kawai.

Malamin y ace akwai abubuwa da dama na yada al’adun muslunci da ilmantarwa, da ma taruka na addini domin karawa juna sani wadanada duk za a iya gudanar da su a masallatai, wanda kuma hakan zai taimaka domin nan wurin da musulmi suke zuwa kullum har sau biyar a rana.

Daga karshe ya yi kiira ga limamai da su zama mas bayar da gudunmawa wajen fadakar da msuuli kan hakikanin abin da musulunci ya koyar, da kuma kaucewa duk wani abin da zai batawa musulunci suna a duniya.

3589368


captcha