Kwamishinan ya bayyana cewa, sun samu kurafi da dama daga iyayen yara kan yadda ake takura musu da kuma nuna musu bangaranci a kan banbancin addini, a kan haka suka dauki mataki fuskantar wannan lamari.
Ya ci gaba da cewa, iyayen yara sun sanar da su cewa, ana tilasta yayansu cire hijabin musluncia duk lokacin dasuka zo makaranta, ko kuma a tilasta su rike wani kati na musamman da ke nuna cewa an bas u izinin saka hijiabin a cikin makarantar.
Jami'in ya ce irin wadannan matakai sun hannun riga da dokokin da ke cikin kundin tsarin mulkin kasar Afirka ta kudu, wanda ya bayar da izinin yin addini ga kowane mutuma cikin kasar, a kan haka ya ce sun janye wannan doka kuma ba za su taba amincewa da wani abu makamancin haka ba.