Kmafanin dillancin labaran iqna ya nakalto
daga shafin sadarwa na jaridar Indepent ta kasar Birtaniya cewa,a lokacin da
yake halartar taron saka hannayen jari na kasashen ketare a Riyad, Muhammad bin
Salman dan gidan sarkin masarautar Al Saud ya yi alkawalin kakakbe hannun masu
tsatsauran na kasar a cikin ahrkokin mulki.
Yace sun bata shekaru fiye da 30 suna ta jayayya akan akidu wanda kuma hakan ba zai taba kawo akrshe ba,a kan haka dole ne akawo karshen tsatsauran ra'ayin akida a cikin harkokin tafiyar da mulkin gidan sarautar kasar.
Kamar yadda kuam yace madadin tsatsauran ra'ayi, za su rungumi matsakaicin ra'ayi a cikin lamurransu a shekaru masu.
Sai ga dukaknin alamu wasu na da shakku kan wannan furuci da wanann matashi dan shekaru 32 ya yi, domin kuwa sa;on tsatsauran ra'ayi shi ne abin da turawan Birtaniya suka gina gidan sarautar saudiyya akansa, domin shagaltar da msuulmi da wasu kanan abubuwa su yi ta jayayya a kansu suna kafirta junansu da jifar junansu da shirka da bidi'a da sauransu, wanda kuam shi enabin da masarautar Saudiyya take yadawa a cikin kasashen musulmi.
Kamar yadda shi kansa Muhamamd Bin Salman bai fita daga hakan ba, domin kuwa yana da hannu dumu-dumua cikin kisan kiyashin da gwamnatin Saudiyya ke yia akn dubban kananna yara da mata a Yemen, kuma yana da hannu wajen taimaka ma 'yan ta'addan wahabiyawa irin su IS da makanatansu da suke yaki a Syria da wasu kasashen larabawa.