IQNA

An Girmama Wadanda Suka Nuna Kwazo A gasar Kur'ani A Masar

23:49 - July 04, 2018
Lambar Labari: 3482806
Bangaren kasa da kasa, an girmama wasu daga makaranta kur'ani da suka nuna kwazoa gasar Kur'ani a masar tare da halartar Mahmud Kamal Dali gwamnan lardin dali na Jizah.

 

Kamfanin dillancin labaran iqna ya habarta cewa, shafin Bawabah news ya habarta cewa kimanin dalibai 35 suka samu nasarar lashe gasar kur'ani da aka gudanar a lardin Jiza na kasar masar wadanda suka samu karramawa ta musamman.

An gudanar da gasar ne bisa kulawar cibiyar Azhar inda sheikh Abdullah Hesham ya jagoranci gasar wadda aka gudanara  yankin Umraniya na gundumar Jizah.

Mahmud kamal Dali da shekh Hesham Abdullah da kuma wasu jami'ai da malamai sun halarci wannan wuri tare da mika kyautukan da aka yi tanadi ga wadanda suka nuna kwazo.

3727025

 

 

 

 

 

captcha