IQNA

Oman Za Ta Bude Ofishin Jakadanci A Falastine

0:01 - June 28, 2019
Lambar Labari: 3483780
Kasar Oman ta sanar da cewa ta kudiri aniyar bude ofishin jakadanci a Palestine domin jaddada goyon bayanta ga al’ummar Falastinu.

Kamfanin dillancin labaran iqna ya habarta cewa,a  cikin wani bayani bayani da ma’aikatar harkokin wajen kasar Oman ta fitar a jiya, ta sanar da cewa, tana shirin bude ofishin jakadanci a Palestine domin nuna cikakken bayanta ga falastinawa.

Bayanin ya ce yanzu haka wata tagawar Oman na shirin tafiya birnin Ramallah na Falastine domin far shirye-shiryen bude ofishin jakadancin.

Wannan mataki na Oman na zuwa ne a daidai lokacin da wasu daga cikin kasashen larabawa suka shagaltu a birnin Manama na Bahrain domin tattauna shirin yarjejeniyar karni, wanda ke nufin mika Falastinu ga mamayar Isra’ila a hukuamnce.

 

3822687

 

Abubuwan Da Ya Shafa: iqna kamfanin dillancin labaran iqna oman
captcha