IQNA

Mutane 5 Sun Mutu A Kokarin Kubtar Da Wasu Da Aka yi Garkuwa Da Su A Johannesburg

23:54 - July 11, 2020
Lambar Labari: 3484974
Tehran (IQNA) akalla mutane 5 ne suka rasa rayukansu a wata musara wuta a Johannesburg a  kasar Afirka ta kudu a lokacin da aka yi garkuwa da wasu.

Shafin yada labarai na alnashrah ya abyar da rahoton cewa, a yau Asabar mutane 5 ne suka rasa rayukansu a wata musara wuta a Johannesburg a  kasar Afirka ta kudu a lokacin da aka yi garkuwa da wasu a birnin.

Yan sanda sun ce an yi gaekuwa da mutane a unnguwar Zobkom da ke cikin birnin na Johannesburg, kuma bayan mutuwar mutane biyar shida sun samu raunuka.

Haka anan kuma bayanin na ‘yan sanda ya ce baya ga haka an samu tarin makamai da wasu abubuwa masu tarwatsewa tare da ‘yan bindigar da suka yi garkuwar da mutane.

3909947

 

captcha