Shafin yada labarai na alnashrah ya abyar da rahoton cewa, a yau Asabar mutane 5 ne suka rasa rayukansu a wata musara wuta a Johannesburg a kasar Afirka ta kudu a lokacin da aka yi garkuwa da wasu a birnin.
Yan sanda sun ce an yi gaekuwa da mutane a unnguwar Zobkom da ke cikin birnin na Johannesburg, kuma bayan mutuwar mutane biyar shida sun samu raunuka.
Haka anan kuma bayanin na ‘yan sanda ya ce baya ga haka an samu tarin makamai da wasu abubuwa masu tarwatsewa tare da ‘yan bindigar da suka yi garkuwar da mutane.