Shafin punchng ya bayar da rahoton cewa, a cikin bayanin da majalisar koli ta musulmin Najeriya wato The Nigerian Supreme Council for Islamic Affairs ta fitar ta bayyana cewa, bisa la’akari da irin mawuyacin da ake ciki a wannans hekara, musulmi su kauracewa gudunar da manyan taruka a lokacin bukukuwan babbar salla.
Haka nan kuma bayanin ya ce; ganin cewa a shekarar bana maniyya daga Najeriya ba su samu damar tafiya sauke farali ba, a kan hakan mutane za su iya yin amfanin da kudin da suka yi niyyar aikin hajji domin gudanar da ayyukan alhairi da taimakama jama’a marrasa galihu a lokacin idin babbar salla.
Majalisar ta NSCIA ta ce; yanayin da ake ciki yanayi da ba a saba da irinsa ba, a kan haka dole ne a kiyaye ka’idoji na kiwon lafiya domin kare kai daga kamuwa da cutar corona, ko kuma yada ta ga wasu.
Najeriya dai ita ce kasa mafi yawan jama’a a nahiyar Afirka baki daya, inda kimanin mutane miliyan dari biyu suke rayuwa a kasar.