IQNA

Musulmi Mali Sun Gangamin Nuna Goyon Baya Ga Manzon Allah

22:58 - November 02, 2020
Lambar Labari: 3485330
Tehran (IQNA) musulmin kasar Mali sun gudanar da jerin gwano domin tir da keta alfarmar manzon Allah da aka yi a  kasar Faransa.

Tashar TRT ta bayar da rahoton cewa, a  yau dubban musulmin kasar Mali sun gudanar da jerin gwano domin tir da keta alfarmar manzon Allah da aka yi a  kasar Faransa a cikin kwanakin nan.

Masu gangamins un yi Allawadai da shugaban kasar Farasa wanda ya goyi bayan jaridar da ke watsa zanen batunci a kan manzon Allah, tare da yin kira ga Faransa da ta gaggauta janye sojojin kimanin 5,100 da suke jibge a cikin kasar ta Mali da sunan yaki da ta’addanci.

3932790

 

captcha