Tashar TRT ta bayar da rahoton cewa, a yau dubban musulmin kasar Mali sun gudanar da jerin gwano domin tir da keta alfarmar manzon Allah da aka yi a kasar Faransa a cikin kwanakin nan.
Masu gangamins un yi Allawadai da shugaban kasar Farasa wanda ya goyi bayan jaridar da ke watsa zanen batunci a kan manzon Allah, tare da yin kira ga Faransa da ta gaggauta janye sojojin kimanin 5,100 da suke jibge a cikin kasar ta Mali da sunan yaki da ta’addanci.