IQNA

An Fara Gasar Kur’ani Ta Duniya A Kasar Masar

22:58 - February 15, 2021
1
Lambar Labari: 3485653
Tehran (IQNA) an fara gudanr da gasar kur’ani ta duniya ta yankin Port Saeed a kasar Masar.

Tashar Al-shuruq ta bayar da rahoton cewa, a yau Litinin an fara gudanar da gasar kur’ani ta duniya ta yankin Port Saeed a kasar Masar tare da halartar malamai da kuma alkalan gasar gami da makaranta da mahardata.

Tun a jiya ne kwaitin kula da gasar ya fara gudanar da zama, tare da halartar wakilan cibiyar Azhar, da kuma Sheikh Abdulfattah Tarouti da wasu daga cikin malamai.

A zaman farko da aka fara a yau, an gudanar da karatu domin tunawa da Sheikh Khalil Al-husari.

A gasar dai mahardata 52 ne daga kasashe 22 na duniya za su kara da juna, inda daga karshe za a fitar da wadanda suka fi nuna kwazo a kowane bangaren domin ba su kyautuka na musamman.

3954159

 

 

 

Wanda Aka Watsa: 1
Ana Cikin Dubawa: 0
Ba A Iya Watsa Shi: 0
Buhari yunusa
0
0
Allah yasa muga karshen gasar lafiya
captcha