IQNA

Dakarun Yemen Sun Sake Kai Harin Mayar Da Martani Kan Masarautar Saudiyya

23:50 - March 04, 2021
Lambar Labari: 3485714
Tehran (IQNA) sojojin kasar Yemen da kuma dakarun sa kai na kabilun larabawan kasar sun kai wani harin ramuwar gayya a yau a kan masarautar Al Saud.

Majiyar sojojin kasar Yemen ta bayyana cewa sojojin kasar sun cilla makamai masu linzami kan kamfanin man fetur na Aramco da ke birnin Jidda na bakin tekun maliya a kasar Saudiya.

Kakakin sojojin kasar Burgediya Janar Yahyah Saree yana fadar haka a safiyar yau Alhamis ya kuma kara da cewa, hadin guiwan sojojin kasar sun cilla makamai masu linzami samfurin Quds-2 kan kayakin kamfanin Aramco na kasar Sudiya a birnin Jidda.

Kafin haka dai sojojin Yemen sun kai irin wadannan hare-hare a kan kamfanin na Aramco a cikin watan Nuwamban shekarar da ta gabata, inda ta jawo asarori masu yawa ga kamfanin.

Hare-Haren daukar fansar dai suna zuwa ne a daidai lokacin da gwamnatin Saudiyya take kara tsananta hare-harenta ta sama da kasa a kan al’ummar kasar Yemen.

 

3957534

 

 

 

 

 

 

 

captcha