IQNA

An Rufe Filin Jirgi Na San'a Yeman Samakon Munanen Hare-Haren Jiragen Yakin Saudiyya Suka Kai Kansa

20:45 - December 21, 2021
Lambar Labari: 3486712
Tehran (IQNA) Wani jami'in gwamnatin Sana'a a kasar Yemen ya sanar da cewa, an dakatar da gudanar da aikin filin jirgin Sana'a sakamakon hare-haren da jiragen yakin Saudiyya suka kaddmar a kan filin jirgin saman na Sanaa.

Kamfanin dillancin labaran Anatoli ya bayar da rahoton cewa, Kungiyar Ansarullah ta kasar Yemen ta sanar da cewa, bayan harin da jiragen yakin kawancen Saudiyya suka kai a filin jirgin saman birnin Sanaa a daren jiya, an rufe filin sauka da tashin jiragen saman gaba daya, sannan kuma an dakatar da dukkan jiragen agaji na MDD da sauran jiragen jin kai sauka da tashi a wurin.

Raed Jabal mataimakin babban daraktan hukumar kula da zirga-zirgar jiragen sama na gwamnatin ceto kasar Yemen ya bayyana cewa: jiragen yakin Saudiyya sun yi ruwan bama-bamai kai tsaye a filin jiragen sama na Sana'a da daddare, sakamakon haka aikin filin jirgin ya tsaya  gaba daya.
 
Ya kuma jaddada cewa, manufar Saudiyya a wannan harin ita ce hana kai kayan agaji ga al'ummar Yemen da kuma hana jiragen Majalisar Dinkin Duniya da kungiyoyin kasa da kasa da ke aiki a kasar ta Yemen.
 
Ya kuma yi kira ga Majalisar Dinkin Duniya da ta dauki matakin gaggawa don dakile hare-haren da kawancen Saudiyya ke kai wa a filin jirgin saman Sanaa, wanda ya kawo cikas ga ayyukansa.
 
Rundunar kawancen Saudiyya ta sanar a cikin wata sanarwa da ta fitar a yammacin jiya cewa ta kai harin bam a wurare shida a filin jirgin saman Sanaa. 
 

 

 

 
captcha