Kamfanin dillancin labaran iqna ya habarta cewa, ya nakalto daga shafin sadarwa na yanar gizo na al-Qastal cewa, likitocin asibitin na Quds ba su bar wuraren aikinsu ba duk da barazanar da Isra’ila ke yi musu.
Ma'aikatan jinya na asibitin al-Quds da ke Gaza sun sanar da cewa ba za su bar wannan wuri ba saboda barazanar da sojojin yahudawan sahyoniya suke yi na kai harin bam a asibitin.
A wata hira da Al Jazeera, babban darektan ma'aikatar kiwon lafiya ta Gaza ya bayyana cewa: Dole ne mu ci gaba da aikinmu har zuwa lokacin karshe. Ba za mu taɓa barin wannan wurin ba.
Asibitoci a zirin Gaza a halin yanzu suna cike da 'yan gudun hijirar Falasdinu.
Za ku iya kallon asibitin al-Quds a Gaza, wanda ke cike da mata da yara da suka rasa matsugunansu.