IQNA

Gina masallaci a wani sabon kauyen musulmi a Najeriya

19:24 - August 16, 2024
Lambar Labari: 3491707
IQNA - Cibiyar ‘Life for Africa’ ce ta gina masallacin “Syedah Zulikha” ga mazauna kauyukan a Najeriya, wadanda a kwanan nan suka musulunta.

Cibiyar  Turkiyya ta "Life for Africa" ​​ne suka gina masallacin "Sideh Zuleikha" ga mutanen kauyen Dulong a Najeriya.

Dukkan mutanen wannan kauyen sun musulunta kwanan nan inda suka koma addinin musulunci daga addinin Kiristanci.

An buga hoton bidiyon yadda ake gina wannan masallaci a yanar gizo, wanda zaku iya kallo a kasa:

Najeriya kasa ce da ke yammacin Afirka mai yawan jama'a miliyan 230 sannan Ingilishi a matsayin harshen hukuma. Fiye da kashi 50 cikin dari na al’ummar kasar musulmi, wadanda suka fi yawa a arewacin kasar, sai kuma a kudancin kasar mabiya addinin kirista sun fi yawa.

 

 

4231626

 

 

captcha