IQNA

Magoya Bayan Harka islamiyya A Najeriya Sun Yi Allawadai Da Cire Wa Mata Hijabi Da 'Yan Sanda Suka Yi

17:33 - September 02, 2024
Lambar Labari: 3491799
IQNA - Magoya bayan Harka Islamiyya a Najeriya sun gudanar da jerin gwano a birane daban-daban na kasar domin nuna rashin amincewa da kuma yin tir da Allawadai da cire wa mata musulmi hijabi da 'yan sanda suka yi.

kafofin yada labaran Najeriya sun bayar da rahotanni da cewa, Magoya bayan Harka Islamiyya a Najeriya sun gudanar da jerin gwano a birane daban-daban na kasar domin nuna rashin amincewa da kuma yin tir da Allawadai da cire wa mata musulmi hijabi da 'yan sanda suka yi a ranar da suka gudanar da tattakin arbaeen a birnin Abuja.

Majiyoyin Harka Islamiyya sun bayyana cewa, magoya bayan Harkar sun gudanar da jerin gwano na tattakin arbaeen a birnin Abuja, yayin da jami'an tsaro na 'yan sanda suka auka musu da duka da harba barkonon tsohuwa a kansa.

A nasu bangaren jami'an 'yan sanda sun zargi magoya bayan Harka da kai musu hari da jifar jami'ansu da duwatsu, da kona musu motoci gami da kashe 'yan sanda biyu a yayin tattakin.

To sai dai majiyoyin Harka Islamiyya sun karyata wannan zargi, tare da bayyana cewa jami'an 'yan sandan suka fara auka musu a lokacin da suke jerin gwano na lumana, kuma basu da hannu a kona motocin 'yansanda da kuma kisan jami'an 'yan samda biyu da ake zarginsu da aikatawa.

 

4234543

 

captcha