Kamfanin dillancin labaran iqna ya habarta cewa, ya nakalto daga shafin sadarwa na yanar gizo na Al Bayan cewa, an bude wannan baje kolin ne a ranar Litinin 9 ga watan Oktoba da nufin kiyaye al'adu da abubuwan tarihi na kur'ani da ilimin kur'ani a zauren majalisar kur'ani mai tsarki ta Sharjah wanda kuma zai ci gaba har zuwa gobe 12 ga watan Oktoba.
Kimanin rubuce-rubucen ayoyin kur'ani kusan 20 da ba kasafai ake samu ba, aka bayyana su ga jama'a a wannan baje koli ba, kuma wadannan kur'ani sun yi tashe tun fiye da shekaru dubu da suka gabata da kuma karni na biyu da na uku na Hijira.
Wannan tarin ya ba da damar ziyartar taskokin kur’ani da kuma sanin ilimin kur’ani da al’adu ga masu sha’awa da masu ziyara, kuma ta hanyar halartar baje kolin, maziyartan za su karfafa iliminsu na ilimomin kur’ani da tarihi da wayewa ta hanyar ziyartar kur’ani masu kayatarwa.
Babban sakataren majalissar kur'ani mai tsarki ta Sharjah Abdullah Khalaf Al-Hosni ya bayyana cewa: Baje kolin na Sharjah na da nufin karfafa matsayin majalissar kur'ani ta Sharjah wajen yin mu'amala da masu bincike da masana kur'ani, da karfafa hadin gwiwar wannan majalissar da cibiyoyi, jami'o'i da kungiyoyi a fagen ilimi. An shirya takardun kur'ani da rubuce-rubucen da ke taimaka wa 'yan Masarautar zuwa wuraren tarihi na al'adu.