IQNA

Jagoran Hizbullah Ya ce Yaki Da 'Yan Takfiriyyah Ne A gaban Kungiyar

22:45 - October 02, 2014
Lambar Labari: 1456516
Bangaren kasa da kasa, Babban magatakardar Kungiyar Hizbullah ta Lebanon ya bayyana cewa; Fada da ayyukan ta’addacimasu akidar kafirta mutane ne abinda kungiyar ta sanya a gaba a halin yanzu.

Kamfanin dillancin labaran Iqna ya habarta cewa, a yayin ganawar da ya yi da sakataren majalisar koli ta tsaron kasar Iran Ali Shamkani a yau a birnin Beirut, Sayyid Hassan Nasarllah ya  yi ishara da hadin da ake ciki a yanzu a kasa na barazanar ta’addanci wanda ba shi da tamka a cikin wannan yanki, muhimmin abinda kungiyar Hizbullah ta sanya a gaba shi ne fuskantar wannan ta’addancin na masu akidar kafirta mutane da kuma aiko domin hana shi isowa cikin Lebanon.

Sayyid Hassan Nasarllah ya kuma yi ishara da  kokarin da kungiyar ta Hizbullah ta ke yi na ganin an sami zamon lafiya da hadin kan al’ummar kasar. Sayydi Hassan Nasarallah ya kuma jaddada godiya ga Jamhuriyar Musulunci ta iran akan matsayarta na taimakawa gwagwarmaya, tare da cewa; Fuskantar ayyukan ta’addanci na masu akidar kafirta mutane tana da bukatuwa da daukar matakai masu karfi ba wasan kwakwayo ba. A nashi gefen, Sakataren Majalisar tsaron kasar ta Iran Ali Shamkhani ya  yabawa kungiyar HIzbullah akan rawar da ta ke takawa wajen kare kasar Lebanon.

1456011

Abubuwan Da Ya Shafa: Nasrullah
captcha